On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

Yan Najeriya Na Garambaba A Burtaniya Saboda Rashin Samun Aikin Yi

INGILA

‘Yan Najeriya da dama sun shiga cikin halin kunci da yunwa da kuma rashin aikin yi a kasar Burtaniya, bayan da suka biya makudan kudi ga kanfanonin dake shirya tafiye tafiye, domin barin kasar nan , don samun aiyuka masu gwabi a kasar.

Kamar yadda kafar yada labarai ta Sky News ta ruwaito, Ta  baiyana cewar,  ‘yan Najeriyar da suka   baiyana   halin da suke  a ciki, sun ce sun biya ma’aikatan kanfanonin kudi,domin samar masu da bizar  yin aiki a kasar, amma da suka  isa Ingilar  sai suka fahimci babu wuraren aiyukan.

Daya daga cikin mutane,  Ta baiyana cewar  a halin yanzu guzurinta   ya ‘kare  duk da cewar  anyi  mata alkawarin samun aiki.

Kazalika  itama wata mata  ta  ce  sai  da ta biya Fam dubu  10 domin kaita kasar ta Burtaniya  da  zummar samun aiki, amma  Sabanin haka, Da  isar kasar ke  da  wuya,  Ta fahimci cewar  babu  aikin  da  take  nema.