On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

Tinubu Na Jimamin Mutane 86 Da Suka Mutu Sakamakon Gobarar Tankar Mai A Jahar Naija

TINUBU

Adadin wadanda suka mutu sakamakon gobarar tankar mai a wata mahadar titi dake garin Dikko kusa da Suleja a jihar Neja ya karu zuwa 86, yayin da mutane 55 suka samu raunuka, inda suke samun kulawar gaggawa a asibiti.

A ranar Asabar da lamarin ya faru, adadin wadanda suka mutu ya kai 70 sannan guda  50 suka jikkata. Sai dai kuma an kara gano karin gawarwaki tare da yi musu jana’iza a garin na Dikko.

Gwamnan jihar Neja, Mohammed Bago, wanda ya ziyarci wurin da gobarar tankar man ta  faru, ya hana ababen hawa da suke  tahowa  daga  yankin  Maje wucewa ta gadar Dikko.

Shima a nasa bangaren,  shugaban kasa  Bola Tinubu ya bayyana matukar alhininsa  kan ibtila’in da  ya faru,  sannan kuma  ya  umarci  hukumomi da abun ya shafa da su bayar da cikakkiyar kulawa ga wadanda suka samu  ‘kuna, tare da  umartar   hukumar kare  afkuwar  hadurra ta kasa  data  tabbatar ta  dauki matakan kare afkuwar  irin hakan a nan gaba.