On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

Ra'ayoyin Gwamnoni Ya Rabu Kan Karin Albashi Na Wucin Gadi Ga Ma'aikata

Gwamnoni

Ra’ayoyin jahohin kasar sun rabu zuwa gida biyu kan yarjejeniyar da Gwamnatin Tarayya ta cimma da kungiyoyin kwadago na yin Karin naira dubu 35 ga ma’aikatan gwamnatin tarayya.

Yayin da wasu daga cikin jihohin suka ce za su karawa  ma’aikatansu daidai da abunda gwamnatin tarayya ta tsara, wasu kuma sun ce tuni sun fara biyan ma’aikatansu Naira 10 kafin yarjejeniyar,  a saboda  haka ba su da wata  alaka da matakin da gwamnatin tarayya  ta dauka.

A yanzu haka  gwamnatin jahar  Enugu da Ondo sun amince su karawa ma’aikatansu naira dubu 35 a yayin da  jihohin Kwara da Adamawa suka ce  sun  fara biyan ma’aikatansu karin naira dubu  10.

A jihohin Kebbi da Neja, gwamnatocin sun ce nan ba da jimawa ba za su zauna da ‘yan majalisar zartarwarsu  domin tantance irin albashin da za a biya ma’aikatan.