On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Peter Obi Ya Musanta Cewar Yana Tattaunawa Da Kwankwaso Da Atiku Domin Kafa Sabuwar Jam'iyya

Dan takarar shugaban kasa a zaben da ya gabata karkashin jam’iyyar Labour, Peter Obi, Ya musanta rade-radin da ake yi na cewar sun tattaunawa tsakaninsu da Atiku Abubakar da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso domin su hade wuri daya, ta yadda zasu samu damar karbar mulki daga hannun jam’iyyar APC mai mulkin kasa, Inda ya bawa ‘yan jam’iyyarsa tabbacin ci gaba da kasancewa a jam’iyyarsa.

Wani rahoto  da aka fitar a ranar Litinin,  ya baiyana  cewar mutanen ukku,  Atiku Abubakar da Peter Obi da kuma Sanata Kwankwaso  na tattaunawa  kan  yadda  zasu yi Hadaka, domin ganin sun wargaza jam’iyyar  APC a zaben shekarar  2027,saboda  zargin cewar  hukuncin da kotu zata yanke  ba zai yi masu dadi ba.

To sai dai Peter Obi ya musanta  rahoton a lokacin da yake jawabi yayin  wani gangamin yakin neman zabe da aka shirya a jihar Edo, Gabanin zaben kananan hukumomin jihar da za’a yi,  Inda  ya ce wasu daga cikin abubuwan da magoya bayansa  zasu rika  ji,  jita-jita ce  kawai.

Dagan an sai yayi kira  ga  masu neman shugabancin kananan hukumomin jihar Edo a karkashin jam’iyyar  sa ta Labour, das u tabbatar sun cika alkawuran d asuka  dauka, idan suka samu nasara.