On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

NLC Ta Ki Amincewa Da Saka Femi Gbajabiamila A Matsayin Mai Shiga Tsakaninsu Da Gwamnati

Gamaiyyar kungiyoyin kwadago na kasa sun nuna rashin amincewar su da saka shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, a matsayin wakilin gwamnatin taraiyya da zasu tattauna dashi kan batutuwan da suka shafi rage radadin janye tallafin man fetir da gwamnatin taraiyya ta yi.

Shugaban kungiyar kwadago na kasa,  Kwamared  Joe  Ajaero  ne ya  tabbatar da haka a  jiya, a yayin wata ziyara  da shugabancin kungiyoyin kwadago suka kai zauren majalisar dattawa.

Ya  ce  aiyuka  sun yiwa  shugaban ma’aikatan  yawa,  wanda hakan yasa  ba lallai ya rika  halartar ganawar  da zasu yi  ba,  Ya kuma koka  kan yadda aka kwashe  kusan watanni biyu  batare  da  anyi wani zama tsakaninsu da kwamitin tsara sabon albashi da  shugaban kasar  ya kafa  ba.

Shima  shugaban kungiyar kwadago ta TUC, Festus  Usifo  ya koka  kan  tafiyar  hawainiya da ake samu dangane da  matakan  rage radadin janye  tallafin man fetir  da gwamnati  ta  yi alkawarin samarwa.

Ya  ce  shugabancin majalisar  dattawa  ya basu tabbacin cewar  zai gana da shugaban kasa  domin ganin an warware  matsalolin ta cikin ruwan sanyi.