On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Najeriya Ce Kan Gaba A Bangaren Masu Zaman Kashe Wando A Duniya

Najeriya ce ke kan gaba a jerin kasashen da suka fi fama da matsalar rashin aikin yi, kamar yadda wata kididdiga ta duniya da aka fitar ta baiyana.

Najeriya ce ke kan gaba da kashi 33  da digo  3  cikin 100 a  bangaren masu zaman kashe wando  sai kuma   kasar  Afirka ta Kudu dake da  kashi 32 da digo 9 cikin 100  yayin da  Iran  ked a   kashi 15 da digo  55 cikin 100.

Rahoton ya ce mafi karancin marasa aikin yi   sune  suke a   kasashe kamar Qatar  da  Cambodia  sai kuma, jamhuriyar  Nijar

A cewar Hukumar Kididdiga ta Kasa, yawan marasa aikin yi a Najeriya ya karu zuwa kashi 33 da digo 30 a rubu'i na hudu na shekarar 2020