On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Mutanen Da Aikin Tagwaita Titin Kano Zuwa Gwarzo Ya Shafa Sun Koka Kan Yi Watsi Da Aikin

TITIN KANO ZUWA GWARZO ZUWA DAYI

Mutanen dake zaune a garuruwan dake kan hanyar Kano zuwa Gwarzo zuwa Dayi ,sunyi kira ga gwamnatin taraiyya data binciki yan kwangilar da ke aikin tagwaita hanyar, wadda aka yi watsi da aikin a halin yanzu.

Idan ba’a manta  ba gwamnatin taraiyya ta kaddamar da aikin tagwaita  hanyar mai tsawon kilomita 82 da digo 3  a ranar  11 ga watan  yunin  2021 akan kudi naira bilyan 62 da milyan 700.

Daya daga cikin jagororin mazauna garuruwan  Alhaji Abdullahi Kanye, ya fadawa manema Labarai cewar kiran  nasu ya zama wajibi  domin gano dalilin da yasa  kanfanin dake kwangilar aikin mai suna CGC Nigeria Ltd  Ya watsi da rabin aikin.

Bincike  ya nuna  cewar an gina  hanyar  ne  tun a zamanin gwamnatin mulkin soja da Ibrahim Badamasi Babangida,  Kuma tun daga lokacin babu wani gyara da aka yi  mata  zuwa yanzu.