On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

Jam'iyyar APC Zata Fara Gangamin Yakin Neman Zabenta A Ranar 28 Ga Satumba

APC

Sakamakon sauyin da aka samu, Jam’iyyar APC mai mulkin kasa, ta sanar da cewa zata fara gangamin yakin neman zabenta na shugaban kasa daga ranar 28 ga watan Satumbar bana.

A yaune ake saran kwamitin gudanarwar jam’iyyar APC na kasa  a karkashin  shugaban jam’iyyar   Sanata Abdullahi Adamu, zai yi wata ganawa ta musamman domin  domin tsayar da matsaya guda  da kuma sanar da lokacin da za’a yi taron kwamitin kolin jam’iyyar na kasa.

A taron  kwamitin na baya da aka yi cikin watan Afrilu ta bawa kwamitin wa’adin kwanaki 90  domin ya  fitar da matsayarsa . Wata majiya daga kwamitin ta baiyana cewa ganawar gaggawar ta zama wajibi domin  baiyana abunda aka tsaya a kai, a karkashin sanata Abdullahi Adamu.