On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

Jagororin Juyin Mulki A Nijar Sunce Ba Zasu Karbi Wakilan Kungiyar ECOWAS Ba

Jagororin juyin mulkin jamhuriyar Nijar, sun ce ba za su amince da kai masu ziyarar manyan jami'an diplomasiyya ba, saboda masu ziyarar zasu iya fuskantar babban hadari.

A yau ne ya kamata wakilai daga kungiyar Ecowas da kungiyar Tarayyar Afirka da kuma Majalisar Dinkin Duniya su   garzaya zuwa kasar  a kokarin da ake na  lalubo bakin zaren sasantawa.

Sai dai shugabannin juyin mulkin sun fadawa  Ecowas cewa takunkumi da barazanar mamaye kasa da  kungiyar  tas saka, sun haifar da fushi daga bangaren  jama'a, a saboda  haka ba za a iya karbar bakuncin tawagar   jami’an a halin yanzu ba.

Rahotanni daga Yamai babban birnin kasar sun ce mutane da dama sun yi maraba da juyin mulkin a matsayin shakar iskar  yanzi , duk da cewa an zabi hambarraren  shugaban kasar  Mohamed Bazoum ta hanyar dimokradiyya.