On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

INEC Zata Kashe Bilyan 18 Wajen Gudanar Zaben Jihohin Imo Da Kogi Da Bayelsa

Bayanan da suka fito daga cikin kudurin daftarin kwarya-kwaryar kasafin kudin bana, da majalisar zartarwa ta kasa ta amince da shi a jiya, ya nuna cewar hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta zata samu naira milyan dubu 18 domin gudanar zaben gwamnonin jihohin Imo da Bayelsa da kuma Kogi.

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin ministan kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arzikin kasa, Atiku Bagudu, wanda  ya zanta da manema Labarai na  fadar  shugaban kasa, kan  abunda taron ya  kunsa.

A wani bangaren kuma, Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta ta  fitar  da bayanan yawan katinan zabe na din-din da aka karba  da kuma  wadanda  ba’a karba  ba a jihohin guda  ukku.

Hukumar  ta  roki masu ruwa  da tsaki  da su kwana da sanin cewar  duk inda aka samu  kuri’ar da aka dangwala a rumfar zabe ta haura adadin katin zaben da aka karba a rumfar  zaben,  to zai kasance  an samu aringinzon kuri’a.