On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Gwamnan Kano Ya Kara Nada Mutane 42 A Matsayin Masu Temaka Masa

A cigaba da gaba da nade-naden mukamai da ya ke yi, Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya nada karin wasu mutane 42 a matsayin masu temaka masa da kuma bashi shawara.

Sanarwar da kakakinsa  Sanusi Bature  ya fitar  a daren jiya, Ya  ce wadanda aka nada kan mukaman, sun hada  da,  Yusuf  Ibrahim Sharada a matsayin babban mataimakin gwamna  kan  bangaren  fasahar  sadarwar zamani.

Kazalika gwamnan ya nada Muhammad Sani Hotoro a matsayin babban mataimakinsa  ta bangaren  kungiyoyin  hadin kai, Sai Barrister  Nura Abdullahi Bagwai a matsayin  babban mataimakinsa a  bangaren shari’a,  Sai Hon Surajo Kanawa a matsayin babban mataimakin gwamna  ta bangaren wayar da kan jama’a a bangaren Kano ta Kudu.

Shi kuwa  Muhammad  Sani Salisu  Riming ado shine babban babban hadimin gwamna  a bangaren wayar da kan jama’a a shiyyar kano ta Arewa, yayin da Nuhu Isa Gawuna zai rike irin wannan matsayi a kano  ta tsakiya da sauran mutane daban daban da gwamnan ya nada kan mukamai na siyasa.