On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

Gwamna Abba Kabir Ya Shigar Da Kararsa Gaban Kotun Daukaka Kara

Gwamna Abba

To yanzu haka dai a hukumance, Gwamna Abba Kabir Yusuf na nan jahar Kano ya garzaya gaban kotun daukaka kara domin kalubalantar hukuncin da kotun sauraren kararrakin zaben gwamna ta yanke na sauke shi daga kan kujerarsa ta gwamnan kano.

Gwamnan ya gabatar da wasu hujjoji har guda 23 a gaban kotun daukaka karar, wanda yake fatan  zata yi amfani dasu  domin soke hukuncin da kotun  kararrakin zaben gwamnan kano ta yanke.

Ya baiyana cewar kotun  ta yi abunda ya sabawa doka, a lokacin da ta dogara da sashi na 71 da kuma 63 na dokar zabe ta kasa  wajen soke  kuri’u  dubu 165 da 616  daga  cikin kuri’un da aka zabe  shi da su.

A cikin kunshin karar  mai shafuka  35, da gwamnan kano da kuma jam’iyyar sa  ta NNPP suka daukaka, sun bukaci kotun daukaka karar data tabbatar dashi a matsayin wanda  ya lashe zaben gwamnan kano na ranar  18 ga watan Maris din bana.