On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Ana Fuskantar Barazanar Karancin Man Fetir Da Tashin Farashinsa

Dillalan Mai sunyi korafin cewar an samu karuwar farashin man fetir da suke sayowa daga Rumbunan ajiyar mai zuwa naira 720 akan kowacce lita daya, A yayin da mafi akasarin rumbunan ajiyar man suka kasance a kulle sakamakon karancin man da ake fuskanta, biyo bayan matsalolin da suka danganci canjin kudaden kasashen waje.

Sun baiyana cewar a saboda  haka  ana cigaba da rufe gidajen mai  da  dama a kowacce rana, wanda hakan kuma zai iya haifar  da matsalar karancin man fetir a  yan watanni masu zuwa  a fadin kasar nan.

Da yake tabbatar da korafin dillalan man, Shugaban kanfanin mai  na  PETROCAM Trading Nig Ltd. Patrick Ilo, Ya ce  man da kanfaninsa  ya sayo har tan  dubu 52 a Talatar data gabata,  ya saye shi ne akan naira 720  kan kowacce  Lita daya, batare da biyan wani tallafin mai a cikinsa ba.

Y ace  a sakamakon tashin farashin man da aka samu a  halin yanzu, farashinsa zai iya kaiwa naira  729 akan kowacce Lita daya  jahar  Legas, idan har da gaske gwamnatin tarayya  ta dena biya tallafin mai.

Ya dora alhakin tashin farashin man, da kalubale na canjin kudi, inda  ya jaddada cewar  har yanzu gwamnatin tarayya  tana biyan tallafin mai  ta bayan fage.