On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

An Sauke Shugaban Wani Asibiti A Kano Saboda Zargin Yin Almundahana

Hukumar kula da asibitoci ta jihar Kano ta umarci shugaban Asibitin kula da masu larurar Mafitsara na Abubakar Imam Dr Atiku Adamu da kuma shugaban Likitoci na Asibitin Dr Kabiru Ahmad, dasu sauka daga kan matsayinsu a nan take, har zuwa lokacin da za’a kamma gudanar da bincike bisa zarginsu da aikata almundahanar kudi.

An dauki matakin ne  biyo bayan  korafe-korafen da aka  samu  wanda  suka da karbar  kudi daga  hannun  marassa  lafiya, da  tura  marassa  lafiya zuwa asibitoci masu zaman kansu   domin yi masu magani ko kuma tiyata, da  kuma zargin aikata  lefin almubazzaranci.

Wata sanarwa mai dauke  dasa hannun  jami’ar hulda da jama’a  ta Hukumar, Samira  Suleiman, Ta  ce  shugaban hukumar,  Dr  Mansur  Mudi Nagoda  ne  ya bada umarnin,  bayan  amincewa da daukar  matakin da kwamishinan lafiya  na jihar Kano, Dr. Abubakar Labaran Yusuf  ya yi.

Sanarwar  ta kuma  baiyana cewar hukumar  ta amince  da yin sauyin wurin aiki  ga  daukacin  ma’aikata da masu   tarbar  marassa  lafiya zuwa wasu  asibitocin, tare da maye  gurbinsu  da wasu batare da bata  loakci ba.