On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

An Dawo Da Shirin Bautar Kasa A Borno Bayan Shafe Shekara 13

Hukumar kula da shirin masu hidimtawa kasa ta fara aikin wayar da kan masu hidimitawa kasa kafin rarraba su zuwa wurare daban daban a karon farko, bayan shafe shekara 13 batare da gudanar da shirin ba, tun bayan da aka dakatar da shi a shekarar 2011, saboda matsaloli na rashin tsaro.

Jami’in kula da shirin a jihar, Mohammed Adamu a lokacin da yake jawabi yayin bukin rantsar da rukunin masu hidimtawa kasar a ranar Talata, ya jinjinawa  gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum saboda namijin kokarinsa  wajen ganin an ci gaba da shirin a jihar.

An yiwa masu bautawa kasar sansani a  kwalejin horas da malaman  larabci  dake jihar, wadda  ke zama  matsagunnin  wucin gadi , a yayin da hadakar jami’an tsaro suka   tsaurara  tsaro a wajen.

Shima a nasa jawabin gwamna Zulum,  ya baiyana farin cikinsa  wajen ganin dawowar shirin, inda  ya ce  yunkurin  ya sake  tabbatar da dawowar zaman lafiya da tsaro a jihar  bayan shafe  shekaru da dama  tana fama da  matsalar  mayakan tada kayar  baya.